Daga Ibrahim Muhammad Kano

Dan takarar majalisar tarayya na qaramar hukumar Fagge a jam’iyyar ADC Kwamared Haruna Kabiru Wakili ya jajantawa yan Kasuawar katin kwari  bisa iftila’i da ya samesu na ambaliyar ruwa da jawo  lalata dukiyoyi masu tarin  yawa.

Ya kuma yi irin wannan jaje ga yan  kasuwar Titin Bairut  suma bisa  matsalar da aka samu a kasuwar na  rushewar wani  gini da ya jawo asarar rai da raunata mutane.

Kwamared Haruna Wakili  ya yi fatan wadanda abin ya shafa  Allah ya mayar musu  da alheri ya kuma bunkasa abinda aka rasa.

Dan takarar majalisar na tarayyar dai ya yi irin wannan jaje ga al’ummar yankin yan mata Gabas dake yankin Fagge   bisa iftila’i na zaizayar kasa da ambaliyar ruwa daya shafe su da  fatan Allah ya mayar musu da alkhairi ya kawo musu  dauki na gaggawa kuma ya mayar da alkhairi ga  dukkan al,’umma da ambsliyar ruwan ya shafa.

Kwamared Haruna ya yi kira ga mahukunta akan su kai dauki dan tallafawa wadanda sukayi asara, sannan a dauki matakai dan  yin kandagarki ga aukuwar abin nan gaba.

Kwamared Haruna yace idan ya zama wakilin al’ummar Fagge a tarayya zai yi kokarin daukar matakan  ganin an kyautata yanayin magudanan ruwa da kuma kawo dauki ga matsalar zaizayar kasa a wasu sassan yankin.

 

 

 

 

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *